Connect with us

Labarai

Yau za a yi Sallar Gani a Kano karon farko a tarihin Masarautar Jihar

Published

on

A yau ne ‎Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu zai gudanar da hawan sallar gani a cikin birnin Kano wanda zai kasance karo na farko a tarihin Masarautar Kano.

‎Rahotanni daga fadar Sarkin sunce za’a gudanar da hawan ne a yau Asabar da kuma gobe Lahadi inda Mai Martaba Sarkin zai fito domin halartar bukukuwan hawan sallar gani.

‎Hawan sallar gani wata al’ada ce da ake gudanarwa a wasu masarautun arewacin Najeriya.

‎Anasa ran wannan hawan sallar gani gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf zai kasance babban bako a yayi hawan.

‎Hawan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirye shiryen bukukuwan Maulidin Annabi Muhammad (SAW).

Ku kasance da mu a shafin mu na Facebook a FreedomradioNigeria domin kallan hawan kai tsaye da kuma sauraro tashoshin mu wato Freedom Radio da Dala fm a yammacin wannan rana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!