Connect with us

Labarai

Yan Sandan Abuja na shirin tsaurara mataki kan masu karya dokokin hanya

Published

on

Rundunar ’Yan Sandan Abuja za ta tsaurara mataki kan direbobin da aron hannu yayin tuƙi da sauran masu karya dokokin hanya.

 

Rundunar ta bayyana hakan ne ta cikin sanarwar da Jami’ar ta hulɗa da Jama’a SP Josephine Adeh, ta fitar a ranar Lahadi.

 

Sanarwar ta ce, Kwamishinan ’yan Sandan Abuja, Ahmed Muhammed Sanusi, ya umarci jami’an Rundunar su tsaurara matakan tabbatar da bin dokokin hanya tare da kama wa da gurfanar da masu karya dokokin.

 

Ya kuma umarci jami’an su ƙara sintiri da sa ido a manyan tituna da wuraren cunkoson ababen hawa domin kama masu yi wa mutane fashi a irin waɗannan wurare.

 

Kwamishinan ya gargaɗi jami’an da za su gudanar da aikin kan karɓar kuɗi, cin zarafi ko tsoratar da jama’a, yana mai cewa duk wanda ya karya umarnin zai fuskanci matakin ladabtarwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!