Connect with us

Labarai

Neja: Manoma biyar sun Rasu sakamakon kifewar Kwale-kwale

Published

on

Manoma biyar, maza huɗu da mace ɗaya, sun mutu bayan wani kwale-kwale ya kife a Kogin Kudi, a Ƙaramar Hukumar Katcha ta Jihar Neja da ke arewacin Nijeriya.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar a ƙauyen Shaba-Woshi-Kpaya, da ke gundumar Edotsu, a cewar ganau.

Wani mazaunin yankin, Muhammadu Dan-Asabe, ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa mutanen suna kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu ne lokacin da kwale-kwalen ya kife.

 

Daraktan Yaɗa Labarai da Ayyuka na Musamman na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr

 

Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce waɗanda abin ya rutsa da su suna tafiya ne daga ƙauyensu zuwa gonakinsu lokacin da kwale-kwalen ya kife.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!