Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Za a gina cibiyar gwajin Corona a Jigawa

Published

on

Gwamnatin jihar jigawa tace tana aikin gina cibiyar gwajin cutar Coronavirus da zata fara aiki nan da makonni biyu masu zuwa.

Gwamnan jihar Alh. Muhd Abubakar ne ya sanar da haka ga manema Labarai da yammacin ranar talatar nan a gidan Gwamnatin jihar dake Dutse.

Gwamnan yace sun dauki wannan mataki ne sakamakon kalubalen da jihar ke fama dashi na rashin cibiyar gwaji wadda hakan ke janyo mata jinkirin gano masu dauke da cutar.

Karin labarai:

Uwargida ta haifi ‘yan hudu a Jigawa

Ma’aikatan lafiya sun kamu da Corona a Jigawa

Kazalika gwamna Badaru yace wannan cibiya za ayi mata matsugunni ne a wani sabon sashe dake cikin babban asibitin Dutse, wato Dutse (General Hospital).

Wakilinmu Muhd Aminu Umar Shuwajo ya rawaito gwamnan na cewa wannan cibiya koda bayan cutar Coronavirus, cibiyar za ta cigaba da gwajin cutuka irinsu Ebola da lassa da dai sauran cutuka masu yaduwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!