Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: Wadanda suka warke daga Corona a Kano sun zarce na Abuja

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da sallamar mutane 63 da suka warke daga cutar Covid-19 a jihar.

Wannan adadi dai ya sanya adadin wadanda suka warke a Kano ya zarce na birnin tarayya Abuja.

A alkaluman hukumar dakile yaduwar cutuka ta kasa NCDC na ranar Litinin yace mutane 53 ne suka warke daga cutar ta Corona a birnin Abuja wanda shi ne gari na biyu da cutar ta fara bulla a kasarnan.

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano sanar an shafinta na Twitter cewa zuwa ranar Litinin mutane 666 ne aka gano suna dauke da cutar a Kano.

32 daga ciki sun rasu, sai 63 da aka sallama bayan sun warke.

A ranar Litinin dinnan ne gwamnatin Kano ta tsawaita dokar kulle da zaman gida a jihar har tsawon mako guda.

Karin labarai:

Ganduje ya gana da sarakuna kan Coronavirus

Yadda cibiyar gwajin Corona ta Dangote ke aiki a Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!