Labarai
Za a kammala aikin hanyar Abuja zuwa Kaduna da Kano a Nuwamban bana- Dave Umahi

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna da Kano nan da watan Nuwamba bana.
Ministan Ayyuka, Sanata Dave Umahi, ne ya bayyana hakan lokacin da shugabannin Kungiyar Dalibai na kasa, NANS, karkashin jagorancin shugaban kungiyar, Babatunde Akinteye, suka kai masa ziyara a Abuja.
Sanata Umahi ya ce gwamnatin tarayya ta kashe sama da naira biliyan 200 wajen aikin, inda ya kara da cewa sama da kashi 80 cikin 100 na kudin aikin da ake gudanarwa a halin yanzu an biya.
Ministan ya kuma nuna damuwa kan yadda ake lalatawa tare da satar kayayyakin da ake amfani da su wajen gina manyan hanyoyin gwamnatin tarayya.
Umahi ya ce gwamnatin tarayya za ta kara zuba jami’an tsaron da za su rika kula da babbar hanyar Abuja–Kaduna–Zariya–Kano, domin kare ta daga masu lalata kayayyakin aikin.
You must be logged in to post a comment Login