Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Za’a fuskanci farin abinci a jihohin Kano da Lagos – NBS

Published

on

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ta ce karancin abinci zai karu a jihohin Lagos da Kano da Abuja da kuma Jihar Rivers sakamakon cutar Corona.

Hakan a cikin rahoton da hukumar ta fitar a jiya Litinin tana mai bayyana cewa jihohin hudu su ne za su fuskanci karancin abinci sakamakon illolin da cutar Corona tayi.

Ta cikin rahoton hukumar, ta ce jihohin Abuja da Rivers wadanda kaso saba’in da biyu na al’ummar su basa iya cin abinci sau uku a rana tun farkon bullar cutar Corona zuwa yanzu.

NBS ta kuma bayyana cewa adadin mutanen da ke sanya kan su a kangin bauta ya karo a kaso biyu na wannan shekara sama da watan Yuni da Yuli da kuma kafin bullar cutar Corona.

Yayin da hukumar ta ce adadin ma’aikata a birnin tarayya Abuja ya ragu da kaso sha hudu, yayin da a jijojin Kano da River al’ummar cikin su ke gudanar da ayyukan noma da masana’antu fiye da kafin bullar Corona a kasar nan.

NBS ta cikin rahoton ta ce a yanzu al’ummar kasar nan na fuskantar rayuwa cikin kangin bauta fiye da shekarar 2018 da 2019

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!