Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

An fara binciken ‘yan sandan da ake zargi da baiwa masu safarar kwayoyi gudummuwa

Published

on

An fara binciken ‘yan sandan da ake zargi da baiwa masu safarar kwayoyi gudummuwa

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sauyawa baki dayan jami’anta dake aikin yaki da miyagun kwayoyi na hadin gwiwa da sauran jami’an tsaro wurin aiki.

Kwamishinan ‘yan sandan na jihar Kano CP. Ahmed Iliyasu ne ya bada umarnin sauya musu wurin aikin, biyo bayan korafin da abokanan aikin su na hukumar KAROTA su ka yi na cewa idan suka kama kayan maye a yankin Sabon Gari dake nan Kano, sai su kuma ‘yan sandan su basu umarnin su sake shi.

Cikin wata tattaunawa da Freedom Radio tayi da kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwa al’amarin inda ya bayyana mana cewa baya ga sauyawa ‘yan sandan da ake zargi wurin aiki, tuni aka fara bincikar su kan lamarin domin daukar mataki bisa umarnin kwamishinan ‘yan sanda na jihar.

Allah ya kyauta.

RUBUTU MAI ALAKA:

‘Yansanda sun kama wani matashi mai garkuwa da mutane

Abinda yasa ‘yansanda suka cafke Sadiya Haruna

Yadda ‘Yansandan Kano suka cafke wadanda suka kone magidanci

Rundunar yan sandan Kano ta yi holin mutane 116 da ake zargi da manyan laifuka

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!