Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wani bazawari ya fito da hanyar karbar waya a hannun mata

Published

on

Shi dai wannan mutum ya kasance  yana karbar waya ne a hannu zauarawa da “yan mata ne da sunan soyayya a unguwar yakasai cikin birnin Kano.

Asirin mutumin ya tonu ne a lokacin da ya karbi wayar wani baiwan Allah da sunan zai dan saka layin sa yayi waya bayan kuma ya karbi wayar sai ya gudu da ita ba’a kara ganin sa ba sai bayan wasu ‘yan kwanaki inda shi kuma yace bazeyadda ba sai ya biya shi dalilin da yasa hakan takai da zuwa ofishin ‘yansanda da yake kwalli.

Bincike da ‘yansanda sukayi ya tabbatar da cewa shi daman wannan mutun halinsa kenan domin kuwa bai tsaya a kan Mata ba harma da Maza don kuwa har Kaninsa yayi wa haka.

‘Yan sanda sun kama mai damfarar matasa

‘Yan yahoo sun damfari loba boy

Hukumar EFCC ta cafke masu kamfanin boge da bindigu a Kano

Tuni dai aka gabatar da wannan matashi a gaban kotun shari’ar Musulunci dake cikin Jihar Kano mai lamba 2 inda shi kuma ya musanta faruwar lamari.

Mai shari’a ya bada umarnin da a cigaba da tsare shi wannan mutun har zuwa lokacin da za’a cigaba da Shari’a.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!