Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Rundunar ‘yan sanda ta samar da tsaro don tunkarar zaben da za’a a Kano

Published

on

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta ce zata samar da ingantaccen tsaro a dukkannin kananan hukumomi tara da za’a sake gudanar da zabe a ranar 25 ga watan da muke ciki, domin ganin an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.

Kwamishinan yansandan jihar Kano CP Habu Sani ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da Hukumar zabe ta kasa reshen Jihar kano ta shirya a yau Talata, a shirye shiryen sake gudanarda zabe a wasu daga cikin kananan hukumomin jihar Kano.

Habu A Sani ya kara da cewa rundunar ‘yansandan jihar Kano ta shirya tsaf domin ganin an gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali da luma , kuma ba zata zuba idanu wasu mutane su tayarwa da jama’a hankali na a lokacin zabe.

Kano: mai amfani da kafafen sada zumunta ya zargi rundunar ‘yan sandan Kano da cin zarafinsa

Jigawa:Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da mutuwar mutane 7 a wani batsari da ya afku

Rundunar ‘yan sanda ta Kano ta yi holin masu yin garkuwa da mutane

Wakilin Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa, hukumomin tsaro daban-daban ne suka halarci taro domin tabbatarwa da hukumar zabe ta Jihar kano shirin su na sake gudanar da zabe a wasu kananan hukumomin jihar Kano guda tara.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!