Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ganduje zai fara gurfanar da iyayen almajirai masu bara a gaban kotu

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yayi alkawarin fara gurfanar da iyayen yaran dake bara a gaban kotu.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sahannun sakataren yada labaran gwamnan Kano Abba Anwar, ta bayyana cewa gwamnan ya bayyana hakan ne yayin taron raba takardun daukar aiki ga malaman da suka bada gudummuwa ta sa kai, ga makarantun Firamare a Kano.

Sabbin malaman makaranta dubu bakwai da dari biyar 7,500 suka karbi takardar daukan aiki daga gwamnatin Kano, a yau Talata.

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yayin da yake raba takardun daukar aiki ga sabbin malaman 25-02-2020

Ganduje ya kara da cewa, gwamnatin sa ta haramta yin bara a Kano baki daya, kuma gwamnati ta shirya tsaf domin gurfanar da iyayen yaran da aka samu suna bara a gaban kotu.

Gwamna Ganduje ya kara da cewa sakamakon tsarin gwamnatin Kano na ilimi kyauta kuma dole, za’a zamanantar da harkar karatu ta tsarin almajirci.

A karshe Gwamnatin Kano ta ce zata rarraba malamai 7,500 da ta dauka zuwa makarantu tsangayu da kuma na boko.

Labarai masu alaka:

Majalisa ta amince Ganduje ya nada sabbin masu ba shi shawara

Ganduje zai dauki likitoci 44 a dukkanin kananan hukumomi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!