Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A sanya dokar gwaji kafin aure – masu Sikila

Published

on

Kungiyar masu fama da cutar sikila a Kano sun nemi gwamnati ta kafa dokar tilasta gwajin jini kafin aure.

Kungiyar ta ce ta hakan ne za a samu nasarar magance yawan masu fama da lalurar sikila a Najeriya.

Shugabar kungiyar, Rukayya Kamal Ibrahim yayin shirin barka da Hantsi na Freedom Rediyo da ya mayar da hankali kan ranar masu lalurar sikila ta duniya, ta ce masu fama da wannan ciwo na cikin mawuyacin hali, don haka akwai bukatar gwamnatoci su tashi tsaye domin shawo kan matsalar.

“Ya kamata gwamnatin Kano da ma Najeriya ta samar da asibitoci na musamman da zasu rika kula da masu cutar sikila, musamman a bangaren basu agajin gaggawa, domin a halin yanzu shine babbar matsalar da muka fama da ita” inji Rukayya Kamal.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!