Connect with us

Labarai

An ceto mutane 16 bayan rushewar wani gini a jihar Kano – Fire Service

Published

on

Aƙalla mutane 16 ne aka ceto da ransu bayan rushewar wani ginin zama a Dan Dishe, Kwanar Yashi, da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano. Daga cikin waɗanda aka ceto, uku an tsamo su cikin halin suma.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya ce jami’an hukumar sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 4:32 na safiyar Asabar, inda aka sanar da su game da rushewar ginin. Ya ce jami’an sun isa wurin, inda suka tarar da ginin mai girman ƙafa 20 da 30 ya rushe.

Hukumar kashe gobara ta ce an miƙa dukkan waɗanda abin ya shafa ga Usman Ibrahim, ɗan’uwan mahaifinsu, domin ci gaba da kula da su. A cewar hukumar, ana ci gaba da bincike domin gano musabbabin rushewar, yayin da ta buƙaci jama’a da su ƙara taka-tsantsan, musamman a lokacin damina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!