Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Zamfara ta karbi kason farko na allurar rigakafin corona

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara ta karbi kason farko na allurar rigakafin cutar ta COVID-19 wanda yawansu yakai dubu 55,000 don yiwa kimanin mutane dubu 27,000.

Kwamishinan lafiya na jihar Alhaji Yahaya Muhammad Kanoma ne ya bayyana hakan ga manema labarai lokacin da yake karbar alluran rigakafin.

Kanoma ya ce allurar rigakafin za ta isa a yiwa mutane dubu 27,000 har zagaye biyu.

Ya kuma ce za a fara yiwa ma’aikatan gwamnati, malamai, ‘yan jarida, direbobin motocin haya da sauran su.

A cewar Kanoma tuni gwamnatin jihar ta horar da wasu ma’aikatan da za su kula da aikin allurar duk da cewa jihar Zamfara itace ke da mafi karancin masu dauke da cutar corona a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!