Manyan Labarai
An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/10/Daurawa.jpg)
Wani mutum mai suna Ibrahim Muhammad Jidda mazaunin garin Maiduguri ya bayyana cewa bidiyon nan da ake yadawa kan cewa Sheikh Aminu Daurawa ne ke tikar rawa a wurin taron biki ba gaskiya bane.
A cewar Ibrahim Muhammad Jidda cikin wani faifan sauti da ya saki a shafukan sada zumunta, a ala-hakika ba shi bane domin kuwa lamarin ya faru ne akan idon sa a wani dakin taro mai suna White Arena dake GRA a Maidugurin.
‘Yace mutumin da aka nuno a cikin bidiyon kani ne ga wani dan siyasa a Maiduguri da ya samu halartar bikin, amma sam ba Mallam Daurawa bane sai dai sunyi kama sosai da Mallam Daurawa din.
Saurari cikakken bayanin nasa a kasa:
Tun da farko dai an fara yada wannan bidiyo ne wanda ke nuna wani mutum da wata suna tikar rawa a wurin taron biki inda aka rika yada shi da sunan cewa wai Mallam Daurawa ne ke waccen rawar.
Kalli wasu bayanai da aka wallafa a shafin facebook kan bidiyon a kasa.
Sai dai tuni Shehin malamin ya fito ya karyata labarin.
Rubutu masu alaka:
An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne
Za’a sanyawa unguwannin ‘yan gayu na’ura mai amfani da hasken rana