Connect with us

Labarai

An karɓi sakamakon farko game da sabuwar cutar da ta ɓulla a Kano

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi ƙarin bayani kan sakamakon farko da ta samu daga birnin tarayya Abuja kan cutar da ta ɓulla a wasu yankunan Kano.

Babban jami’in kwamitin kar-ta-kwana mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa na ma’aikatar lafiya ta Kano Dr. Bashir Lawan ya ce, an samu fitowar sakamakon farko game da batun.

Wanda ya nuna cewa, ba zazzaɓin lassa ko cutar shawara ba ce.

Sannan sakamakon binciken ya nuna cewa, cutar ba ta da alaƙa da ruwan rijiyar da ke maƙabartar Ɗandolo.

Yanzu haka akwai sauran samfuri na sinadarin da ake haɗa lemo da sinadarin ɗan tsami wanda ake cigaba da bincike a kansa.

Kuma kawo yanzu an gano cewa, wa’adin amfani da sinadaran ya ƙare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!