Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

An raba sinadarin wanke hannu a Asibitin Murtala

Published

on

Shugaban kungiyar taimakon matasa ta Arewa, KuleChas Arewa kwamrade Abdullahi Aliyu ya yi kira  ga kungiyoyi  masu zaman kansu dasu taimakawa gwamnati a kokarin da take na  yakar cutar Corona.

Abdullahi Aliyu, yace kungiyoyi suna da rawar da zasu taka wajen taimakon  al’umma ba sai gwamnati  ka dai ba.

Abdullahi Aliyu ne ya bayyana haka lokacin da kungiyar su ta yi rabon  kayan wanke hannu da tsafatar sa a  asibitin Murtala.

Ya kara da cewa kungiyar su tana taimakawa asibiti da makarantun da kayan aiki kamar su sinadarin wanke hannu Sanitizer,  domin yakar cutar Corona mai lakabin Covid 19.

Labarai masu alaka.

Dalilan da suka sanya Buk ta musanta bullar cutar Corona

Covid-19: An takaita zirga-zirga a kasuwar kantin Kwari

Yace sun kuma shirya bita  don wayar da kan mutane akan cutar data gallabi  al’ummar duniya dama kasa baki daya.

A nasa jawabin shugaban asibitin Murtala,  Dakta Husaini Muhammad, ya yabawa wannan  kungiya, tare da yi musu alkawarin hadin kai tsakanin Asibitin da kungiyar , tare da gode musu da bisa bada tallafin  kayan wanke hannu.

Shamsu Dau Abdullahi, wakilin mu da ya halarci taron  ya rawaito cewa marasa lafiya da dama ne suka samu wannan tallafi na kayan a kokarin da ake na dakile wannan cuta mai saurin hallaka mutane.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!