Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An rufe wasu cibiyoyin lafiya a Kano – Dakta Tijjani

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta rufe wasu cibiyoyin lafiya 3 sakamakon kin sabunta rijstar su na shekarar 2020.

 

Wannan dai na cikin wata sanarwa da hukumar kula da lafiya da Cibiyoyin lafiya na jihar Kano ta fitar mai dauke da sa hannun sbabban sakataren hukumar Dakta Usman Tijjani Aliyu.

 

Sanarwar ta bayyana cewa an rufe cibiyoyin ne sakamakon rashin cika ka’idojin da hukumar ta sanya na sabubta rijisatarsu a kowacce shekarar.

 

A cewarsa asibitocin da aka rufe sun hadar da asibitin ido da ke kan titin Civic centre da asibitin hakori na Orbit da ke Sabon Titin Mandawari da asibitin hakori na ABC da ke kan titin zariya.

 

Dakta Tijjani Aliyu ya ce daga fara zagayen duban asibitin a farkon makon da muke ciki, hukumar ta rufe asibnitin Baraka da ke unguwar Darmanawa, da asibitin M. D. G. da ke hanyar Ribadu a karamar hukumar Tarauni.

 

A cewarsa matakin rufe su ya biyo bayan sabawa umarnin sabunta rijstar su da hukumar ta umarce su suyi duk shekarar, a don haka za a ci gaba da rufe wuraren har sai sun cika ka’ida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!