Labarai
Ana yunƙurin yiwa ‘yan Najeriya kutse a bankunansu – CBN

Babban bankin Najeriya CBN ya gargaɗi ‘yan ƙasar da su kasance cikin shiri saboda masu kutsen Intanet da ke ta yunƙurin kutse cikin asusun ɗaiɗaikun mutane.
Babban bankin ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ya fitar mai ɗauke da sa hannun muƙaddashiyar harkokin watsa labarai Hakama Sidi Ali a ranar Talata.
CBN ya ce masu kutse na tura wani saƙo na bogi zuwa ga email ko sakon karta kwana na mutane suna cewa daga bankin sakon yake.
A cewa sanarwar akwai cutar da mutane a saƙon inda suke neman mutum ya danna wani link daga nan kuma sai su samu damar shiga cikin asusun.
Daga nan kuma sai su bar me asusun da zargin CBN ya sace masa kudi.
You must be logged in to post a comment Login