Labarai
Iran ta ki amincewa da sake bude mashigar Hormuz

Iran ta ki amincewa da sake bude mashigar Hormuz muddin killacewar da sojojin ruwan Amurka suka yi ya ci gaba, duk da tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta.
Iran din ta kuma ce ta kama jiragen ruwa uku da suka yi yunkurin ketare wannan muhimmin wuri na zirga-zirgar jiragen ruwa.
Kakakin majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya ce ba zai yiwu a bude mashigar ba yayin da ake ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta.
A nasa bangaren, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai ci gaba da tsagaita wutar domin bai wa tattaunawar zaman lafiya karin lokaci.
You must be logged in to post a comment Login