Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ana zargin wani dan KAROTA da dabawa wasu direbobi wuka

Published

on

Rikici ya rincabe tsakanin jami’an hukumar lura da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA da wasu direbobi a sha tale-talen gidan jaridar Triumph.

Sai dai rundunar ‘yan sandan Kano ta ce ana zargin daya daga cikin jami’an KAROTAn da cakawa direbobi biyu wuka.

Kakakin rundunar yan sandan jihar DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce su na gudanar da bincike a kan al’amarin.

Freedom Radio ta yi kokarin jin ta bakin hukumar ta KAROTA domin jin matsayar ta akai, sai dai har zuwa wannan lokaci bamu samu ji daga gare su ba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!