Connect with us

Labarai

Atiku ya ƙalubalanci gwamntin shugaba Tinubu kan tallafin Fetur

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya ƙalubalanci gwamnatin tarayya da ta bayyana wa ’yan Najeriya yadda aka kashe kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin man fetur.

 

A cikin wata sanarwa da babban mataimakinsa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar a madadinsa, Atiku ya ce gwamnati ta cire tallafin tare da neman ’yan Najeriya su jure wahalhalun da hakan ya haifar, bisa alkawarin cewa za a yi amfani da kuɗin wajen ayyukan ci gaba.

 

Atiku ya ce tashin farashin man fetur, sufuri da abinci ya ƙara jefa ’yan Najeriya cikin wahala, yana mai tambayar gwamnati inda kuɗin jama’a suke.

 

Ya kuma ƙalubalanci gwamnatin Tinubu da ta bincike shi idan tana da hujjar aikata ba daidai ba, maimakon ta riƙa maimaita zarge-zargen da suka shafi lokacin da yake mataimakin shugaban ƙasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!