Labarai
Atiku ya yi gargadi kan yunkurin dakatar da yakin neman zabe a wasu sassan Arewa

Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar, ya yi gargadi kan yunkurin dakatar da yakin neman zabe a wasu sassan Arewacin Najeriya da ya ce hakan na iya tauye hakkin kundin tsarin mulki da kuma kara fargabar hana jama’a damar kada kuri’a a daidai lokacin da matsalar tsaro ke kara tsananta.
Martanin Atiku ya biyo bayan rahotannin da ke cewa majalisar dattawa na nazarin yiwuwar dakatar da harkokin siyasa a jihohi takwas da ke fama da karuwar tashe-tashen hankula, a arewacin kasar nan.
Atiku ya ce lamarin abin damuwa ne matuka, yana mai cewa duk da cewa rashin tsaro babbar matsala ce, bai kamata a yi amfani da ita wajen takaita shiga harkokin dimokuradiyya ba.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya jaddada cewa al’ummar Arewa, kamar sauran ‘yan Najeriya, suna da hakkin samun tsaro da kuma cikakkiyar damar shiga harkokin dimokuradiyya.
Madugun adawar ya ce alhakin gwamnati ne ta tabbatar da tsaro, kamar yadda ya kamata a bar ‘yan kasa su yi amfani da hakkokinsu na kasa ba tare da tsoro ko tsangwama ba.
You must be logged in to post a comment Login