Connect with us

Ƙetare

Ba mu da niyyar cutar da Qatar- Majalisar tsaron Iran

Published

on

Majalisar tsaron kasar Iran, ta ce, harin da ta kai sansanonin sojin Amurka da ke cikin Qatar ba shi da niyyar cutar da ƙasar.

 

Ta cikin wata sanarwa da majalisar ta fitar, ta ce Iran za ta ci gaba da martaba dangantakar tarihin da ke tsakaninta da Qatar.

 

Harin baya ɗauke da wani hatsari ga mutanen Qatar, saboda ba ƙasar harin ya nufa ba.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, yawan makamai masu linzamin da aka yi amfani da su a harin sun yi dai-dai da adadin boma-boman da Amurka ta yi amfani da su a cibiyoyin nukiliyar Iran uku.

 

Gwamnatin Qatar dai ta ce, na’urorin kakkaɓo makamanta sun samu nasarar daƙile makaman na Iran.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!