Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bamu dakatar da Kwankwaso ba – Uwar jam’iyyar PDP

Published

on

Jam’iyyar PDP ta ƙasa ta yi watsi da wani labari da ake yaɗawa, na cewa ta kori tsohon Gwamnan Kano Rabi’u Kwankwaso daga jam’iyyar.

Hakan na cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na ƙasa Kola Ologbondiyan ya fitar da yammacin Lahadi.

Sanarwar ta bayyana ƙarara cewa, labarin da ake yaɗawa labari ne na ƙanzon kurege, a don haka ba ta dakatar da Kwankwaso ba.

Jam’iyyar ta jaddada cewa, kundin tsarin mulkin ta ya tanadi matakan da ake bi domin dakatar da mamba a kwamitin zartarwa na ƙasa ba wai kara-zube ba.

Ologbondiyan ya ƙalubalanci masu yaɗa labarin kan su kawo matakan da aka bi domin zartar da wannan mataki.

Jam’iyyar ta PDP ta kuma gargaɗi masu yaɗa wannan labarin da cewa ba zata lamunci hakan ba, domin zai iya taɓa ƙima da mutuncin jam’iyyar.

A wani ci gaban labarin kuma jam’iyyar ta PDP ta ƙaryata labarin cewa ta dakatar da tsohon Gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu.

Jam’iyyar ta ce, ta lura da wani labari mara tushe da ake yaɗawa na cewar ta dakatar da shi.

A ƙarshe PDP ta nemi shugabanni da mambobin ta kan su yi watsi da irin waɗannan labarai, su haɗa kan su domin ciyar da jam’iyyar gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!