Connect with us

Labarai

Benue: Jami’an tsaro sun kubutar da daliban da aka sace a hanyar zuwa jarrabawar JAMB

Published

on

Jami’an tsaro sun yi nasarar kubutar da daliban da aka sace a hanyar zuwa jarrabawar JAMB da sauran fasinjojin a Jihar Benue.

 

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar, Ifeanyi Emenari ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin da yake gabatar da mutane 15 daga cikin waɗanda aka ceto ga Gwamna Hyacinth Alia a fadar gwamnati da ke Makurdi.

 

Ya ce an samu nasarar ceto mutanen ne bayan wani samame na haɗin gwiwar jami’an tsaro, kuma duka mutanen suna cikin ƙoshin lafiya.

 

Kwamishinan ya kuma sanar da kama mutane bakwai da ake zargi da hannu a lamarin, yana mai bayyana hakan a matsayin babban ci gaba a binciken da ake yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!