Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

COVID-19- Amurkawa dubu biyu suka rasa rayukan su

Published

on

Amurkawa dubu biyu ne suka rasa rayukansu cikin kwana guda, sakamakon ci gaba da yaduwar cutar corona.

Kididdiga da jami’ar John Hopkins ta fitar, ta ce, ya zuwa karfe takwas da rabi na daren jiya laraba, alkaluman mutanen da suka mutu cikin awanni ashirin da hudu sun kai dubu biyu.

A cewar jami’ar ta John Hopkins, wannan shine rasa rayuka karo na biyu a jere mafi muni a kasar tun bayan bullar cutar ta covid-19.

Ya zuwa yanzu dai, jimillar wadanda suka mutu a kasar ta amurka sanadiyar cutar corona, ya kai dubu goma sha hudu da dari shida da casa’in da biyar; adadin da ya zarce na kasar spain wanda mutane dubu goma sha hudu da dari biyar da hamsin da biyar suka mutu.

Rahotanni sun ce, ya zuwa yanzu kasar Italiya ce ke kan gaba a yawan adadin wadanda suka rasa rayukansu sanadiyar cutar ta corona, inda mutane dubu goma sha bakwai da dari shida da sittin da tara suka rasu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!