Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

COVID-19: Bikin kakar wasanni ka iya zama barazana ga lafiyar al’umma

Published

on

Masana kiwon lafiya sun gargadi hukumar kwallon kafa ta Najeriya kan batun gudanar da gasar bikin kakar wasanni ta shekarar 2020 yayin da ya rage saura makwanni uku a fara.

Za dai a gudanar da bikin kakar wasannin ne a ranar goma sha hudu zuwa ranar ashirin da takwas ga watan Faburairu a garin Benin dake jihar Edo.

Masana kiwon lafiya na ganin cewa gudanar da gasar ka’iya zama barazana ga lafiyar al’umma duba da yadda annobar Coronavirus data dawo kuma take ci gaba da yin kamari a fadin kasar nan.

Rahoto na cewa, kawo zuwa ranar 26 ga watan Janairu yawan wadanda suka kamu da COVID-19 a Najeriya ya kai 122,996 yayin da kuma cutar ta kashe mutane 1,509.

Ana dai tsammanin ‘yan wasa da jami’ai kimanin 15,000 za su hallaci wajen gudanar da bikin kakar wasanni a jihar ta Edo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!