Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ganduje ya gana da sarakuna kan Coronavirus

Published

on

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya gana da sarakunan gargajiyar biyar masu daraja ta daya na jihar kan annobar Covid-19.
Yayin ganawar da ta gudana a fadar gwamnatin Kano, Gwamna Ganduje ya nemi sarakunan da su rubanya ayyukan da sukeyi na wayar da kan al’umma kan cutar Corona.

Hoto yayin ganawar

Hoto yayin ganawar

Wakiliyarmu ta fadar gwamnatin Kano Zahra’u Nasir ta rawaito mana cewa gwamnan yace ya kamata sarakunan su jajirce wajen ilimantar da al’umma domin bin dokokin jami’an lafiya game da cutar da kuma zuwa wajen gwaji ga wanda aka gani da alamar cutar.
Da yake jawabi Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga al’umma kan su dage wajen neman gafarar ubangiji tare da rika taimakawa marasa karfi a wannan yanayi da ake ciki.

Karin labarai:

Yadda cibiyar gwajin Corona ta Dangote ke aiki a Kano

Mutane 50 sun warke daga Corona a Kano
Har ila yau wakiliyar mu Zahrau Nasir ta ruwaito cewa mai baiwa ministan lafiya shawara akan cutar Corona a Kano Farfesa Abdussalam Nasidi ya ce cikin sati biyu da zuwansu Kano an samu nasara sai dai akwai bukatar karin gudummuwar sarakunan gargajiyar kan yakar cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!