Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

KWALARA: Sama da mutane dubu 30 ne suka kamu da cutar a Najeriya – NCDC

Published

on

Cibiyar dakile yaɗuwar cututtuka ta ƙasa NCDC ta ce, adadin waɗanda suka kamu da cutar kwalara a ƙasar nan ya kai dubu talatin da uku da ɗari shida da sittin daya a jihohi ashirin da uku.

Haka kuma wasu dari tara da talatin da uku sun rasa rayukan su saboda cutar ta kwalara.

Ministan muhalli Muhammad Mahmud Abubakar ne ya tabbatar da wannan adadi, yayin da yake yiwa manema labarai ƙarin bayani jiya a Abuja.

Ya ce, akwai buƙatar gaggauta sanar da ‘yan Najeriya yadda cutar ke sake bazuwa da kuma irin matakan da ya kamata su ɗauka don kare kan su.

Gwamnatin Kaduna ta bullo da binciken gida-gida don kare al’umma daga kamuwa da cutuka masu yaduwa

Ya ƙara da cewa a yanzu jihohi 22  ne cutar tayi ƙamari, ciki har da birnin tarayya Abuja, da Benue, Delta, Zamfara, Gombe, Bayelsa, Kogi, Sokoto, Bauchi, da Kano.

Sauran su ne, Kaduna, Plateau, Kebbi, Cross River, Neja, Nasarawa, Jigawa, Yobe, Kwara, Enugu, Borno, Kastina, sai Adamawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!