Ƙetare
Dakarun juyin juya halin Iran sun mutu a yunkurin su na kwance nakiyoyi

Kamfanin dillancin labarai na Fars a Iran ya bayar da rahoton cewa dakarun juyin juha halin ƙasar 14 ne suka mutu a daren da ya gabata sakamakon fashewar wata nakiya da aka dasa lokacin yaƙin ƙasar da Amurka da Isra’ila.
A cewar Fars, ofishin hulda da jama’a na rundunar IRGC, a lardin Zanjan inda lamarin ya faru, ya ce dakarun rundunar 14 ne suka mutu, yayin da biyu suka jikkata a lokacin ƙoƙarin dakarun rundunar na kwance nakiyar.
Mataimakin gwamnan Zanjan ya ce za a rufe duka ma’aikatun gwamnati da bankuna a lardin a ranar Lahadi domin jana’izar dakarun.
You must be logged in to post a comment Login