Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dalilin da ya sa ƙungiyar ƙwadago ta kasa (NLC) ta janye yajin aiki a Kaduna

Published

on

Ƙungiyar ƙwadago ta kasa (NLC) ta janye yajin aikin kwanaki biyar (5) da ta fara a jihar Kaduna

 

Tun farko dai gamayyar ƙungiyoyin ƙwadagon ƙarkashin jagorancin shugaban ƙungiyar NLC Ayuba Wabba sun jagorancin ma’aikata a jihar ta Kaduna wajen gudanar da zanga-zangar adawa da salon da gwamna El-Rufai ya dauka na korar ma’aikata.

 

Tun farko dai gwamna Nasir El-Rufai ya ƙalubalanci ƴan ƙwadagon da cewa zanga-zangar da suke yi da yajin aikin ba zai sa gwamnatin jihar ta sauya matsayinta kan batun ba.

 

Sai dai da ya ke zantawa da manema labarai a daren jiya laraba shugaban ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC) kwamared Ayuba Wabba ya ce ƙungiyar ta janye yajin aikin da ta fara.

 

Ya ce sun dau wannan mataki ne ganin cewa gwmanatin tarayya ta dau alkwarin shiga tsakanin don sasanta ɓangarorin biyu

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!