Connect with us

Labarai

Dr. Lawan Ahmed Muhammad Sani ya zama sabon Sarkin Gumel na 17

Published

on

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya naɗa Dr. Lawan Ahmed Muhammad Sani a matsayin sabon Sarkin Gumel na 17, bayan rasuwar mahaifinsa, Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II.

Sanarwar da Sakataren Gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim ya fitar, ta ce naɗin ya biyo bayan shawarar masu zaɓen sarki na masarautar Gumel da Majalisar sarakunan Jihar Jigawa.

Mahaifin sabon sarkin ya rasu ne ranar Alhamis, 3 ga Satumba, 2026, bayan shafe shekaru 46 yana mulkin masarautar Gumel.

Kafin naɗinsa, Dr. Lawan Ahmed Muhammad Sani shi ne Chiroman Gumel, kuma yana aiki a matsayin daraktan Tsaron Intanet na Hukumar NITDA.

Gwamna Namadi ya kuma gode wa masu zaɓen sarki da sarakunan Hadejia, Kazaure, Ringim da Dutse bisa gudunmawarsu wajen zaɓen sabon Sarkin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!