Ƙetare
Mutane 23 sun mutu yayin da 113 suka kamu da cutar kwalara a Sudan

Ana fargabar mutuwar mutane ashirin da uku, yayin da fiye da dari uku da goma suka kamu da cutar kwalara ko kuma ake zargin sun kamu da ita, a wasu yankuna biyu na Kordofan ta yamma a Sudan.
Kungiyar agaji ta Dar Hamar Emergency Room ce ta bayyana hakan, tana mai cewa cutar ta fi kamari a yankunan Humeir da Hilla Hussein.
Kungiyar ta ce a Humeir, ana kula da mutane 120 da ake zargin sun kamu da kwalara, inda mutane 11 suka mutu.
A Hilla Hussein kuwa, an samu sama da mutane 190 da suka kamu da cutar, yayin da 12 suka mutu.
Kungiyar ta kuma yi gargadin cewa cibiyoyin kiwon lafiya na fama da Karancin magunguna da ruwan jinya, lamarin da ke kara ta’azzara matsalar.
Haka kuma, ta ce karancin abinci ya yi tsanani, har wasu iyalai ke amfani da abincin dabbobi wajen ciyar da ’ya’yansu.
Kungiyar ta yi kira ga hukumomin lafiya da kungiyoyin agaji da su gaggauta kai magunguna da kayan abinci ga mutanen yankin.
You must be logged in to post a comment Login