Labarai
Sojoji sun kashe yan ta’adda 152 tare da kama wasu 142

Rundunar Operation Hadin Kai ta ce dakarunta sun halaka ’yan ta’adda 152, tare da kama wasu 142, yayin da 219 suka mika wuya a ayyukan da aka gudanar a arewa maso gabashin kasar nan cikin watan Agusta na shekarar 2026.
Ta cikin wata sanarwa rundunar ta ce ta kuma kai hare-haren sama 10, tare da lalata wasu bama-bamai tara na IED.
Haka kuma, sojojin sun kwato makamai da abubuwan fashewa 58, da harsasai 1,184, baya ga wasu kayan aiki da ake zargin ’yan Boko Haram da ISWAP ne ke amfani da su.
Rahoton ya ce an gudanar da ayyukan ne ta hanyar hare-haren kasa da sama, tattara bayanan sirri da kuma karfafa masu tayar da kayar baya su mika wuya, domin rage karfinsu da kuma dakile hanyoyin samun kayan aiki.
You must be logged in to post a comment Login