Connect with us

Labarai

Ebola ta kashe mutane 2,011 a Kongo DR

Published

on

Cutar Ebola ta kashe mutane 2,011 a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, yayin da adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar ya kai 4,381.

Hukumomin lafiya sun ce annobar, wadda aka sanar a hukumance a ranar 15 ga Mayun 2026, na yaduwa cikin sauri fiye da yadda aka taba gani a baya. Ana kuma zargin cewa cutar ta fara yaduwa tun watanni kafin a sanar da bullarta a hukumance.

Annobar ta shafi larduna biyar, kuma masana kiwon lafiya na fuskantar kalubale wajen dakile ta saboda rikice-rikicen tsaro, karancin kayayyakin kiwon lafiya da kuma wahalar gano mutanen da suka yi mu’amala da masu dauke da cutar.

Wannan dai shi ne annobar Ebola mafi muni da Kongo ta fuskanta tun bayan wadda ta faru a shekarar 2018 zuwa 2020, kuma ta zama ta biyu mafi girma a tarihin duniya.

*Washington Post*

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!