Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje ya ƙaddamar da ma’aikatar kula da harkokin addinin

Published

on

Da safiyar yau Litinin ne gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ƙaddamar da ma’aikatar lura da al’amuran addinin musulunci a gidan Murtala dake nan Kano.

Gwamna Abdullahi Ganduje ya ce, ma’aikatar zata riƙa kula da hukumomin da ke kula da harkokin addinin musulunci da kuma ɓangaren musuluntar da maguzawa tare da inganta mu’amala tsakanin musulmi da waɗanda ba musulmi ba don samun zaman lafiya.

Ya kuma ce, ma’aikatar zata riƙa shirya kasafin kuɗin da zata kashe a duk shekara.

Haka kuma, gwamnan ya buƙaci ma’aikatan dake ƙarƙashin ma’aikatar da su ci gaba da bada haɗin kai wajen tafiyar da ayyukan ma’aikatar yadda ya kamata.

Da yake jawabi a yayin ƙaddamar da ma’aikatar kwamishinan addinai na Kano, Muhammad Tahar Adam ya ce, wannan rana ce mai tarihi, kasancewar ba a taɓa samun ma’aikatar da gwamna ya je bude ta da kansa ba a cewarsa.

Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta rawaito kwamishinan na cewa yanzu haka shekarar ma’aikatar guda da fara aiki, kuma zata ɗora da ayyukan ta wajen tabbatar da ci gaban addinin musulunci a Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!