Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Yan jarida sun samu horo kan aiki da Corona a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata cigaba da baiwa yan jaridu goyon baya musamman wajen kare kansu daga cutar Corona yayin gudanar da ayyukansu.

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan a ranar asabar lokacin gudanar da taron bita ga yan jaridu guda 100 akan yadda zasu kare kansu daga kamuwa daga Corona yayin gudanar da ayyukansu.

Ya ce ‘yan jaridu suna taimakawa a wannan yaki da akeyi da wannan cuta adon haka ya zama lallai su samu kariya daga kamuwa da cutar ta Corona.

Labarai masu alaka:

Da gaske za ayi gwajin maganin Corona a Kano?

Ganduje ya bude cibiyar killace mata masu Corona a Kano

Da yake jawabi shugaban kwamitin ministan lafiya kan cutar Corona a Kano Dakta Nasir Sani Gwarzo cewa yayi kasancewar yan jaridu suna cikin hatsarin kamuwa da cutar adon haka ya zama lallai a ilmantar dasu yadda zasu kare kansu.

Abbas Ibrahim shine shugaban kungiyar yan jaridu reshen jihar Kano ya ce wannan horarwa zata taimakawa yan jaridun wajen yin ayyukansu cikin kariya.

Wakiliyar mu ta fadar Gwamnatin Kano Zahrau Nasir ta ruwaito cewa jami’an lafiya daga fannoni daban-daban ne suka yi ta gudanar da makalolin kariyar kai ga yan jaridu daga cutar ta Covid-19.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!