Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Gobara ta hallaka ƙananan yara ƴan makaranta 20 a Nijar

Published

on

A ƙalla ƙananan yara ɗalibai ashirin ne suka ƙone ƙurmus, a wata gobara da ta tashi a wata makaranta da ke babban birinin Yamai na jamhuriyar Nijar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa gobarar ta tashi ne da yammacin jiya Talata, a makarantar Kongolba da ke Unguwar Ɗanladi a Yamai.

Wakilin Freedom Radio a Yamai Ishu Mamman ya ce, an gina makarantar nw da zana, wanda hakan ya sanya wutar ta riƙa ci babu ƙaƙƙautawa, kafin daga bisani jami’an kashe gobara su kawo ɗauki.

Ya ci gaba da cewa, dukkan kujerun zaman ɗalibai da kayyakin makarantar sun ƙone ƙurmus, kuma tuni al’umma suka shiga jimami kan lamarin.

Sai dai har kawo lokacin da muke haɗa wannan rahoto hukuma a ƙasar ba ta ce komai ba a kai.

Hotunan yadda lamarin ya faru.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!