Labarai
Gobara ta hallaka Uwa da ‘Ya’yanta mata 3 a Yobe

Wata mummunar Gobara ta tashi a Rugar Audu Badali da ke karamar hukumar Karasuwa a jihar Yobe, inda ta hallaka wata mata da ‘ya’yanta uku.
Wadanda suka rasa rayukansu suka hada da Bilkisu, matar Mallam Bukar, da ‘ya’yanta Zainab, Hafsat da Salamatu.
Bayan faruwar lamarin, an yi jana’izar wadanda suka rasu bisa tsarin addinin Musulunci, yayin da gobarar ta lalata gidan iyalan tare da dukiyoyinsu, lamarin da ya bar wadanda suka tsira daga cikin iyalan ba tare da matsuguni ba.
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, SEMA, ta kai ziyara domin tantance irin barnar da gobarar ta yi da kuma gano bukatun gaggawa na iyalan.
You must be logged in to post a comment Login