Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 60 a jihar Neja

Published

on

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane da dama bayan sun kai hari kan wani masallaci da kauyukan da ke kewaye da shi a yankin Dekara, ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Neja.

 

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya ce maharan sun fara kai hari kauyukan Gidan-Zana da Kpenya kafin su kutsa cikin masallacin Kpenya da misalin ƙarfe biyu na rana ranar Juma’a. Mazauna yankin sun ce an yi garkuwa da sama da mutum 60, duk da cewa ba a tabbatar da adadin ba. Wani da ya tsira daga harin ya zargi ƙungiyar Lakurawa da kai harin.

 

Kafar yada labarai ta Al’jazeera ta ruwaito cewa, A halin yanzu jami’an tsaro sun tura runduna ta haɗin gwiwa domin gudanar da bincike da aikin ceto. Mazauna yankin sun kuma ce maharan sun sake dawowa a jiya Asabar, tare da dasa nakiyoyi a hanyar fita daga Dekara, inda wata mota da ke ɗauke da wani mutum da iyalinsa ta taka wata nakiyar, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!