Labaran Kano
Gwamnan Kano ya zabi Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin sa

Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya tura sunan Alhaji Murtala Sule Garo zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin tantancewa da amincewa da shi a matsayin mataimakin gwamna.
Hakan na cikin wata sanarwar da Sakataren Yada Labaran gwamnan, Malam Mustapha Muhammad ya fitar a tsakar daren yau Laraba 22 ga watan Afrilu 2026.
Sanarwar ta bayyana cewa zabar matakin ya yi daidai da sashe na 191(3) na kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya ba gwamna damar nada mataimaki idan an samu gurbi.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa kujerar ta zama babu kowa ne bayan murabus din da tsohon mataimakin gwamna, Comrade Abdussalam Gwarzo ya yi a ranar 27 ga watan Maris 2026.
Murtala Sule Garo mai shekaru 48 ya taba rike mukamai daban-daban a gwamnati da siyasa, ciki har da kwamishina baya ga shugaban karamar hukuma.
You must be logged in to post a comment Login