Labarai
Gwamnatin Kano ta bayyana ranar Talata a matsayin hutun sabuwar shekara Musulunci
Gwamnatin Kano ta bayyana gobe Talata daya ga watan Muharram Hijira ta 1448 a matsayin ranar hutu ga ma’aikata.
Hakan na cikin sanarwar da Daraktar ayyuka Hajiya Safiyya Ali Sulaiman ta fitar a madadin shugabar ma’aikata ta Kano
A cewar sanarwar bayar da hutun na zuwa ne sakamakon shigowar da watan musulunci zai yi daga gobe Talata 16 ga watan Yunin 2026 da muke ciki.
Ta cikin sanarwar gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusif ya bukaci ma’aikatan da su yi amfani da hutun wajen yiwa Kano addu’oin zaman Lafiya da karuwar arziki mai dorewa.

You must be logged in to post a comment Login