Labarai
Gwamnatin Kano ta bukaci matasan jihar da shiga harkokin shugabanci

Kwamishinan ma’aikatar Albarkatun Ruwa Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar Kano Dr Dahiru Muhammad Hashim ne ya bayyana hakan a yayin taron da gwamnatin ta shirya na kaddamar da kungiyar “sabon fata” wato (renewed hope) agenda da ya gudana gidan gwamnatin Kano.
Dr. Dahiru da ya kasance shugaban kungiyar a jihar Kano ya ce wajibi ne matasa su shiga harkokin siyasa, domin samun damar kawo cigaba ga al’ummar Najeriya.
Ya kuma kara da cewa Gwamnatin Kano za ta cigaba da hada kai da Gwamnatin tarayya wajen cigaba da samar da ayyukan raya kasa kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya yi tanadi.
You must be logged in to post a comment Login