Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano za ta binciki yadda kananan hukumomi ke kashe kudaden tsaro

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ba Kwamitinta mai kula da harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu umarnin gudanar da bincike kan yadda dukkanin kananan hukumomi 44 ke kashe kudaden tsaro, kuma ta umurce su da su mika rahoton su cikin makonni biyu.

 

Hakan ya biyo bayan kudurin gaggawa da dan majalisa mai wakiltar Ghari da Tsanyawa, Garba Yau’u Gwarmai, ya gabatar.

 

Yayin gabatar da kudurin, Garba Ya’u Gwarmai, ya bayyana damuwarsa kan tabarbarewar tsaro a yankin Ƴan Kamaye da ke Karamar Hukumar Tsanyawa, inda ‘yan bindiga ake zargi suka kai hari wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

 

Dan majalisar ya ce, maharan da ake zaton sun fito daga Jihar Katsina, sun mamaye al’ummar kusan makonni 3 zuwa 4 da suka gabata, inda suka kashe sama da mutane 8, ciki har da mace mai ciki da ‘ya’yanta biyu. Ya kara da cewa an kuma kashe manoma 5 a wannan hari.

 

Kudurin dai, ya samu goyon bayan bulaliyar majalisar, Muddasir Ibrahim zawaciki mai wakiltar Kumbotso da har ma da sauran wasu cikin mambobin majalisar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!