Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano za ta dauki mataki kan sayar da filayen da aka ware domin inganta Muhalli.

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta dauki matakan da suka dace domin hana sayar da wani fili da ma’aikatu da hukumomi ke amfani da shi wajen yaki da kwararowar hamada da kuma matsalolin sauyin yanayi.

Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Juma’a 08 ga watan Agustan 2026.

 

Ya ce gwamnatin jihar ba ta goyon bayan duk wani yunkuri na sayar da filin, wanda ya ce yana da matukar muhimmanci wajen gudanar da ayyukan kare muhalli da dakile illolin sauyin yanayi.

Dakta Dahiru Hashim ya ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa kadarar ba ta fada hannun wasu mutane ta hanyar da ba ta dace ba.

Ya kara da cewa ma’aikatu da hukumomi da dama, musamman wadanda ke da alhakin yaki da kwararowar hamada da sauyin yanayi, na amfani da wajen wajen gudanar da ayyukansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!