Labarai
Shugabannin Yarbawa a Arewa sun bukaci Tinubu ya kara kaimi wajen rage talauci

Kungiyar sarakunan Yarbawa da shugabanninsu da ke zaune a jihohin Arewa 19 da Abuja, ta bukaci gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kara kaimi wajen rage talauci a kasar.
Shugaban kungiyar, Alhaji Murtala Adeleke, ya bayyana hakan bayan taron kungiyar da aka gudanar a Abuja. Ya ce duk da cewa gyare-gyaren tattalin arziki na bukatar hakuri, ya kamata gwamnati ta tabbatar da cewa al’umma, musamman wadanda ke karkara, sun amfana da romon dimokuradiyya.
Sai dai kungiyar ta bayyana goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Tinubu, tana mai cewa an samu ci gaba a bangarorin tsaro, ilimi, samar da man fetur da tattalin arziki. Haka kuma ta yaba wa gwamnatin kan kokarin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma inganta jin dadin jami’an tsaro.
You must be logged in to post a comment Login