Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano za ta tallafawa makarantun kimiyya da kayan agaji

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta ci gaba da tallafawa makarantun sakandare na kimiyya da fasaha da kayan aiki da na agaji, domin bunƙasa harkokin ilimi a fannin.

Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Makarantun Kimiyya da Fasaha ta jihar, Farfesa Dahiru Sale Muhammad, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron ƙaddamar da shirin rabon kayan kashe gobara da kayan wasanni ga makarantun.

Ya ce samar da irin waɗannan kayan na daga cikin matakan da ake ɗauka domin inganta yanayin koyarwa da koyo a makarantun kimiyya da fasaha na jihar.

A nasa jawabin, Haya Sufeto Janar na Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Ibrahim Umar Muhammad, ya bayyana matakan da ya kamata a ɗauka domin rage haɗarin iftila’in gobara da kuma kare rayuka da dukiyoyi.

Ya kuma jaddada muhimmancin wayar da kan ɗalibai da ma’aikatan makarantu kan hanyoyin da za su taimaka wajen dakile gobara da kuma matakan gaggawa idan gobara ta tashi.

Wakilinmu, Akilu Musa Garba Diso, ya ruwaito cewa taron ya samu halartar wakilai daga makarantun sakandare na kimiyya da fasaha na jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!