Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babu ranar bude jami’o’i – ASUU

Published

on

Kungiyar malaman jami’o’I ta Najeriya (ASUU) ta ce ba za su koma aji ba, ko da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin bude makarantu, yayin da ake fama da annobar Covid-19.

Shugaban kungiyar, Boidun Ogunyemi a wata hira da manema labarai, ya sake jaddada shawarar da suka bawa gwamnatin Najeriya na kada ta bude makarantu har zuwa shekarar 2021.

Ranar 19 ga watan Maris ne gwamnatin Najeriya ta bayar da umarnin a rufe dukkanin jami’o’in kasar hadi da makarantun sakandire da kuma firamare, bayan da aka samu bullar cutar Coronavirus a kasar.

Sai dai bayan kwanaki kadan da bayar da umarnin ne, ASUU ta fara yajin aikin sai baba ta gani, wanda ta ce har yanzu tana kan bakarta.

ASUU ta ce ta shiga yajin aikin ne saboda shawarar da gwamnatin tarayya ta yanke na hana albashi ga mambobinta da suka yi watsi da sabon tsarin biyan albashin bai daya na IPPIS da gwamnatin ta bullo da shi.

Duk da cewa a yanzu gwamnatin tarayya ta ba da ka’idojin da ta ke son a yi amfani da su ga daliban da za su kammala makaranta a matakan firamare da na sakandire, sai dai babu abinda aka ce game da jami’o’in Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!