Labarai
Sojoji sun kashe wasu manyan jagororin yan bindiga

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka wasu manyan jagororin ‘yan bindiga biyu, Anaruwa da Gomina, tare da wasu mutum bakwai a jerin hare-haren da aka gudanar cikin kwanaki uku a jihohin Zamfara da Katsina.
Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai na rundunar, Sashe na 8 na Operation Fansan Yamma, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa, da ya fitar aka raba ga manema labarai
An kuma bayyana cewa Anaruwa ƙanin shahararren jagoran ‘yan bindiga ne, Kachalla Idi Aiki.
Laftanar Kanal Olaniyi ya ƙara da cewa a farkon farmakin, dakarun sun yi arangama da ‘yan ta’addan a kan hanyar Bagega zuwa Anka, inda aka yi musayar wuta mai tsanani tsakanin ɓangarorin biyu.
You must be logged in to post a comment Login