Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta gargadi ma’aikatan lafiya da ke ƙin zuwa aiki

Published

on

Gwamnatin Jihar Zamfara ta gargadi ma’aikatan lafiya kan rashin zuwa aiki tare da yin barazanar ɗaukar matakan ladabtarwa ga duk wanda aka samu da sakaci a wurin aikinsa.

Kwamishinar Lafiya ta jihar, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, ce ta bayyana hakan ga manema labarai.

Gwamnati ba za ta lamunci duk wani abu da zai kawo cikas ga ingantaccen aikin kiwon lafiya ba.

Ta bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba cibiyoyin lafiya a sassan jihar, inda ta jaddada aniyar gwamnati na inganta ayyukan kiwon lafiya da samar da ingantattun ayyuka ga al’umma.

A yayin ziyarar, kwamishinar ta nuna rashin gamsuwa da yanayin tsaftar Babban Asibitin Gusau, tare da umartar kamfanin da ke kula da tsaftar wajen ya gyara aikinsa cikin gaggawa.

Dakta Nafisa Muhammad Maradun ta kuma gargadi masu gudanar da asibitoci masu zaman kansu da su bi ƙa’idojin kiwon lafiya, tana mai cewa duk cibiyar da aka samu tana aiki ƙasa da ƙa’idar da aka tanada za a iya rufe ta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!